20. Ya zama daidai kamar mutum ya ci toka. Manufarsa ta wauta ta ɓatar da shi, har ba yadda za a iya taimakonsa. Ba zai iya ganewa ba, gunkin da ya riƙe a hannunsa ba allah ba ne ko kaɗan.
21. Ubangiji ya ce,“Ka tuna da waɗannan abu, ya Isra'ila,Ka tuna kai bawana ne.Na halicce ka domin ka zama bawana,Ba zan taɓa mantawa da kai ba.
22. Na shafe zunubanka kamar baƙin girgije,Da girgije kuma zan rufe laifofinkaKa komo wurina, ni ne na fanshe ka.”
23. Ku yi sowa ta farin ciki ya ku sammai!Ku yi sowa ku zurfafan wurare na duniya!Ku yi sowa ta murna, ku duwatsu, da kowane itace na jeji!Ubangiji ya fanshi mutanensa, Isra'ila,Saboda haka ya nuna girmansa.
24. “Ni ne Ubangiji, Mahaliccinku, Mai Fansarku.Ni ne Ubangiji, Mahaliccin dukkan abu.Ni kaɗai na shimfiɗa sammai,Ba wanda ya taimake ni sa'ad da na yi duniya.