Ish 41:1-3 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Allah ya ce,“Ku yi shiru ku kasa kunne gare ni, ku manisantan ƙasashe!Ku yi shiri ku gabatar da ƙararku a ɗakin shari'a.Za ku sami zarafi ku yi magana.Bari mu taru mu ga wanda yake da gaskiya.

2. “Wane ne wannan da ya kawo mai yin nasara daga gabas,Ya kuma sa ya ci nasara a dukan inda ya tafi?Wa ya ba shi nasara a kan sarakuna da al'ummai?Takobinsa ya sassare su sun zama kamar ƙura!Kibansa sun warwatsar da su kamar ƙaiƙayi a gaban iska!

3. Yana biye da kora, yana kuma tafiya lafiya,Da sauri ƙwarai, da ƙyar yake taɓa ƙasa!

Ish 41