4. Zan ba da Masarawa a hannun azzalumi a hannun mugun sarki kuma da zai mallake su. Ni, Ubangiji Mai Runduna, na faɗi wannan.”
5. Ruwan Kogin Nilu zai ƙafe, a hankali kogin zai bushe.
6. Mazaunan kogin za su ji wari sa'ad da yake ƙafewa a hankali. Iwa da jema za su bushe.
7. Dukan amfanin gonakin da aka shuka a gaɓar Kogin Nilu za su bushe, iska ta fyauce su.
8. Duk wanda sana'arsa ta kama kifi ce a Kogin Nilu zai yi ƙugi ya yi kuka, gama ƙugiyoyinsa da tarunansa za su zama marasa amfani.
9. Waɗanda suke yin tufafin lilin za su fid da zuciya,
10. shugabanni da ma'aikata za su karai su kuma damu.