Irm 4:29-31 Littafi Mai Tsarki (HAU)

29. Da jin motsin mahayan dawakai dana maharbaKowane gari zai fashe.Waɗansu za su shiga kurama,Waɗansu kuma su hau kan duwatsu.Dukan birane za su fashe tas,Ba wanda zai zauna a cikinsu.

30. Ya ke da kike kufai marar kowa,Me kike nufi da kika ci ado da mulufi,Kike caɓa ado da kayan zinariya,Kika sa wa idanunki tozali ram?Kin yi kwalliyarki a banza,Abokan sha'anin karuwancinki sunraina ki,Ranki suke nema.

31. Na ji kuka kamar na mace wadda takenaƙuda,Na ji nishi kamar na mace a lokacinhaihuwarta ta fari,Na ji kukan 'yar Sihiyona tanakyakyari,Tana miƙa hannuwanta tana cewa,“Wayyo ni kaina, gama ina suma agaban masu kisankai!”

Irm 4