Irm 18:20-23 Littafi Mai Tsarki (HAU)

20. Daidai ne a rama alheri damugunta?Duk da haka sun kafa wa raina tarko.Ka tuna yadda na tsaya a gabanka,Na yi maganar alheri a kansu,Domin ka janye fushinka daga garesu.

21. Saboda haka ka kawo wa 'ya'yansuyunwa,Ka bashe su ga takobi,Bari matansu su rasa 'ya'ya,mazansu su mutu,Ka sa annoba ta kashe mazansu,A kashe samarinsu da takobi ayaƙi.

22. Bari a ji kururuwa daga gidajensu,Saboda maharan da ka aika musufarat ɗaya,Gama sun haƙa rami don in fāɗa,Sun kafa wa ƙafafuna tarkuna.

23. Amma ya Ubangiji,Ka san dukan maƙarƙashiyarsu,su kashe ni,Kada ka gafarta musu muguntarsu,kada kuma ka shafe zunubinsudaga gabanka.Ka sa a jefar da su daga gabanka,Ka yi da su sa'ad da kake fushi!”

Irm 18