Irm 14:1-3 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Maganar da Ubangiji ya yi wa Irmiya a kan fari ke nan,

2. “Yahuza tana makoki,Ƙofofin biranenta suna lalacewa,Mutanenta suna kwance a ƙasa,suna makoki,Urushalima tana kuka da babbarmurya.

3. Manyan mutanenta sun aikibarorinsu su ɗebo ruwa.Da suka je maɓuɓɓuga, sai sukatarar ba ruwa.Sai suka koma da tulunansuhaka nan,An kunyatar da su, an ƙasƙantarda su,Suka lulluɓe kansu don kunya.

Irm 14