15. Ku kasa kunne, ku ji,Kada ku yi girmankai, gamaUbangiji ya yi magana.
16. Ku girmama Ubangiji Allahnku,Kafin ya kawo duhu,Kafin kuma ƙafafunku su yi tuntuɓea kan dutse, da duhu duhu,Sa'ad da kuke neman haske, sai yamaishe shi duhu,Ya maishe shi duhu baƙi ƙirin.
17. Amma idan ba za ku ji ba,Raina zai yi kuka a ɓoye sabodagirmankanku,Idanuna za su yi kuka ƙwarai, za suzub da hawaye,Domin an kai garken Ubangiji zuwabauta.