Gal 1:22-24 Littafi Mai Tsarki (HAU)

22. Amma kuwa ikilisiyoyin Almasihu da suke a ƙasar Yahudiya, ba su san ni ido da ido ba tukuna.

23. Sai dai kawai sun ji an ce, “Wanda dā yake tsananta mana, ga shi, a yanzu yana sanar da bangaskiyar nan da dā yake ta rusawa!”

24. Sai suka ɗaukaka Allah saboda ni.

Gal 1