Fit 16:18-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

18. Amma da aka auna da mudu, ta waɗanda suka zarce ba ta yi saura ba, ta waɗanda ba su kai ba, ba ta gaza ba. Kowane mutum ya tattara daidai cinsa.

19. Musa ya ce musu, “Kada wani ya ci, ya bar saura har safiya.”

20. Amma waɗansu ba su kasa kunne ga Musa ba, suka bar saura, har ta kwana, kashegari kuwa ta yi tsutsotsi, ta ruɓe, sai Musa ya yi fushi da su.

Fit 16