6. “Saboda haka Ubangiji Allah ya ce,‘Da yake ka aza kanka mai hikima ne kamar Allah,
7. Don haka zan tura baƙi a kanka,Waɗanda suka fi mugunta cikin sauran al'umma.Za su zare takubansu a kan kyakkyawar hikimarka,Za su ɓara darajarka.
8. Za su jefar da kai cikin rami,Za ka mutu kamar waɗanda suka mutu a tsakiyar teku.