Ez 28:3-7 Littafi Mai Tsarki (HAU)

3. Lalle ka fi Daniyel hikima,Ba asirin da yake ɓoye a gare ka.

4. Ta wurin hikimarka da ganewarka ka samo wa kanka dukiya,Ka tattara zinariya da azurfa a baitulmalinka.

5. Saboda yawan hikimarka na yin kasuwanci, ka ƙara dukiyarka,Sai dukiyarka ta sa zuciyarka ta cika da alfarma.’

6. “Saboda haka Ubangiji Allah ya ce,‘Da yake ka aza kanka mai hikima ne kamar Allah,

7. Don haka zan tura baƙi a kanka,Waɗanda suka fi mugunta cikin sauran al'umma.Za su zare takubansu a kan kyakkyawar hikimarka,Za su ɓara darajarka.

Ez 28