19. Dukan waɗanda suka san ka a cikin al'ummaiZa su gigice saboda masifar da ta auko maka,Za ka zama barazana ga al'ummai,Ba za ka ƙara kasancewa ba har abada.”’
20. Ubangiji ya yi magana da ni kuma, ya ce,
21. “Ɗan mutum, ka fuskanci Sidon, ka yi annabci a kanta.
22. Ka ce, Ubangiji Allah ya ce,‘Duba, ina gāba da ke, ya Sidon,Zan bayyana ikona a cikinki,Za su sani ni ne Ubangiji sa'ad da na hukunta ta,Na bayyana tsarkina a cikinta.
23. Zan aukar mata da annoba da jini a titunanta.Waɗanda za a ji musu rauni da takobiZa su fāɗi matattu a tsakiyarta.Za a tasar mata a kowane waje.Sa'an nan za su sani ni ne Ubangiji.’ ”