Ez 27:1-6 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Sai kuma Ubangiji ya yi magana da ni, ya ce,

2. “Ya kai ɗan mutum, ka yi makoki domin Taya.

3. Ka ce mata, ita wadda take zaune a mashigin teku, wadda take kuma kasuwar mutanen da suke bakin teku, ni Ubangiji Allah na ce,‘Ke Taya, kin ce ke kyakkyawa ce cikakkiya!

4. Teku ta kewaye kan iyakarki,Maginanki sun ƙawata ki.

5. Sun yi katakanki da itacen fir na Senir,Sun sari itacen al'ul daga Lebanon don su yi miki jigon jirgin ruwa.

6. Sun yi matuƙan jirgin ruwanki da katakon itacen oak na Bashan.Sun daɓe jirgin ruwanki da itacen kasharina na bakin tekun Kittim,Sa'an nan sun manne masa hauren giwa.

Ez 27