Esta 2:16-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

16. Sa'ad da aka kai Esta wurin sarki Ahasurus a fādarsa a wata na goma, wato watan Tebet, a shekara ta bakwai ta sarautarsa,

17. sai sarki ya ƙaunaci Esta fiye da dukan sauran matan. Ta kuwa sami alheri da farin jini a wurinsa fiye da sauran budurwan, saboda haka ya sa kambin sarauta a kanta. Ya naɗa ta sarauniya maimakon Bashti.

18. Sarki kuwa ya yi wa sarakunansa da barorinsa ƙasaitaccen biki saboda Esta. Ya kuma ba larduna hutu, ya ba da kyautai da yawa irin na sarauta.

19. Sa'ad da aka tara budurwai a karo na biyu, Mordekai yana zaune a ƙofar sarki.

20. Har yanzu dai Esta ba ta bayyana asalin danginta da mutanenta ba, kamar yadda Mordekai ya umarce ta, gama Esta tana yi wa Mordekai biyayya kamar ta yi tun lokacin da yake renonta.

Esta 2