12. In ruwan ta ƙafe, ita ce za ta fara bushewa,Tun tana ƙanƙana ba ta isa a yanke a yi amfani da ita ba.
13. Marasa tsoron Allah kamar iwan nan suke,Ba su da sa zuciya muddin sun rabu da Allah.
14. Suna dogara ga silin zare, murjin gizo-gizo.
15. Idan suka jingina ga saƙar gizo-gizo, za ta iya tokare su?Idan sun kama ta, za ta taimake su tsayawa?
16. “Mugaye sukan tsiro kamar ciyayi a hasken rana,Ciyayin da sukan yaɗu su cinye gona duka.