10. Amma ka yarda masu hikima na zamanin dā su koya maka,Ka kasa kunne ga abin da za su faɗa.
11. “Iwa ba ta tsirowa inda ba ruwa,Ba a taɓa samunta a ko'ina ba sai a fadama.
12. In ruwan ta ƙafe, ita ce za ta fara bushewa,Tun tana ƙanƙana ba ta isa a yanke a yi amfani da ita ba.
13. Marasa tsoron Allah kamar iwan nan suke,Ba su da sa zuciya muddin sun rabu da Allah.
14. Suna dogara ga silin zare, murjin gizo-gizo.