Ayu 12:8-19 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. Ka roƙi talikan da suke a duniya, da cikin teku, hikimar da suke da ita.

9. Dukansu sun sani ikon Ubangiji ne ya yi su.

10. Allah shi ne yake bi da rayukan talikansa.Numfashin dukan mutane kuwa a ikonsa yake.

11. Amma kamar yadda harsunanku suke jin daɗin ɗanɗanar abinci,Haka nan kuma kunnuwanku suke jin daɗin sauraren kalmomi.

14. Sa'ad da Allah ya rurrushe, wa zai iya sāke ginawa?Wa kuma zai iya fitar da mutumin da Allah ya sa a kurkuku?

15. Akan yi fari sa'ad da Allah ya hana ruwan sama,Rigyawa takan zo sa'ad da ya kwararo ruwa.

16. Allah mai iko ne a kullum kuwa cikin nasara yakeDa macuci, da wanda aka cutar, duk ƙarƙashin ikon Allah suke.

17. Yakan mai da hikimar masu mulki wauta,Yakan mai da shugabanni marasa tunani.

18. Yakan tuɓe sarakuna ya sa su kurkuku.

19. Yakan ƙasƙantar da firistoci da mutane masu iko.

Ayu 12