4. Har abokaina ma, suna ta yi mini dariya yanzu,Suna ta dariya ko da yake ni adali ne marar laifi,Amma akwai lokacin da Allah ya amsa addu'o'ina.
5. Ba ka shan wahalar kome, duk da haka ka maishe ni abin dariya.Ka bugi mutumin da yake gab da fāɗuwa.
6. Amma ɓarayi da marasa tsoronAllah suna zaune cikin salama,Ko da yake ƙarfinsu ne kaɗai allahnsu.
7. “Don haka tsuntsaye da dabbobi sun fi ka sani,Suna da abu mai yawa da za su koya maka.
8. Ka roƙi talikan da suke a duniya, da cikin teku, hikimar da suke da ita.
9. Dukansu sun sani ikon Ubangiji ne ya yi su.
10. Allah shi ne yake bi da rayukan talikansa.Numfashin dukan mutane kuwa a ikonsa yake.
11. Amma kamar yadda harsunanku suke jin daɗin ɗanɗanar abinci,Haka nan kuma kunnuwanku suke jin daɗin sauraren kalmomi.
14. Sa'ad da Allah ya rurrushe, wa zai iya sāke ginawa?Wa kuma zai iya fitar da mutumin da Allah ya sa a kurkuku?
15. Akan yi fari sa'ad da Allah ya hana ruwan sama,Rigyawa takan zo sa'ad da ya kwararo ruwa.
16. Allah mai iko ne a kullum kuwa cikin nasara yakeDa macuci, da wanda aka cutar, duk ƙarƙashin ikon Allah suke.
17. Yakan mai da hikimar masu mulki wauta,Yakan mai da shugabanni marasa tunani.