20. Yakan rufe bakin waɗanda aka amince da su.Yakan kawar da hikimar tsofaffi.
21. Yakan kunyatar da masu iko,Ya hana wa masu mulki ƙarfi.
22. Yakan aika da haske a wuraren da suke da duhu kamar mutuwa.
23. Yakan sa sauran al'ummai su yi ƙarfi su ƙasaita,Sa'an nan ya fatattaka su, ya hallaka su.