40. Suka ce wa Haruna, ‘Ka yi mana gumakan da za su yi mana jagaba, don Musan nan kam, da ya fito da mu daga Masar, ba mu san abin da ya auku a gare shi ba.’
41. A lokacin nan suka ƙera ɗan maraƙi, suka yanka wa gunkin nan hadaya, suka riƙa farin ciki da aikin da suka yi da hannunsu.
42. Saboda haka Allah ya juya musu baya, ya sallame su ga bautar taurari, yadda yake a rubuce a littafin annabawa cewa,‘Ya ku jama'ar Isra'ila,Ni ne kuka yanka wa dabbobi, kuka miƙa wa hadaya,Har shekara arba'in a cikin jeji?
43. Ai, yawo kuka yi da alfarwar Molek,Da surar tauraron gunki Ramfan,Wato surorin nan da kuka ƙera don ku yi musu sujada.Ni kuwa zan kawar da ku a can bayan Babila.’
44. “Dā kakanninmu suna da alfarwar shaida a jeji, irin wadda mai maganar nan da Musa ya umarta a yi, daidai fasalin da ya gani.