16. Sai aka ɗebo su aka mai da su Shekem, aka sa su a kabarin da Ibrahim ya saya da kuɗi azurfa a wurin 'ya'yan Hamor a nan Shekem.
17. “Amma da lokacin cikar alkawarin da Allah ya yi wa Ibrahim ya gabato, jama'ar suka ƙaru, suka yawaita ƙwarai a ƙasar Masar,
18. har aka yi wani sarki a Masar, wanda bai san ko wane ne Yusufu ba.
19. Wannan sarki kuwa ya cuci kabilarmu, yana gwada wa kakanninmu tasku, yana sawa a yar da jariransu, don kada su rayu.
20. A lokacin nan ne aka haifi Musa, yaro kyakkyawan gaske. Sai aka rene shi wata uku a gidan ubansa.