A.m. 3:3-7 Littafi Mai Tsarki (HAU)

3. Da ganin Bitrus da Yahaya suna shiga Haikalin, ya roƙe su sadaka.

4. Bitrus kuwa ya zuba masu ido, tare da Yahaya, ya ce, “Dube mu.”

5. Sai kuwa duk hankalinsa ya koma a kansu, da tsammanin samun wani abu a gunsu.

6. Amma Bitrus ya ce, “Kuɗi kam, ba ni da su, amma abin da nake da shi, shi zan ba ka. Da sunan Yesu Almasihu Banazare, yi tafiya.”

7. Sai Bitrus ya kama hannunsa na dama, ya tashe shi. Nan tāke ƙafafunsa da wuyan sawunsa suka yi ƙarfi.

A.m. 3