A.m. 3:17-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

17. “To, yanzu 'yan'uwa, na sani da jahilci kuka yi haka, kamar yadda shugabanninku ma suka yi.

18. Amma ta haka Allah ya cika faɗar da ya riga ya yi ta bakin annabawa duka, cewa Almasihunsa zai sha wuya.

19. Saboda haka sai ku tuba, ku juyo, domin a shafe zunubanku, Ubangiji kuma kansa ya riƙa wartsakar da ku,

20. ya kuma aiko da Almasihun da aka ƙaddara muku tun dā, wato Yesu,

A.m. 3