A.m. 21:31-36 Littafi Mai Tsarki (HAU)

31. Suna neman kashe shi ke nan, sai labari ya kai ga shugaban ƙungiyar yaƙi, wai Urushalima duk ta hargitse.

32. A nan tāke ya ɗibi soja da jarumawa, suka ruga zuwa wajensu. Su kuwa da ganin shugaban da soja suka daina dūkan Bulus.

33. Sai shugaban ya matsa kusa ya kama Bulus, ya yi umarni a ɗaure shi da sarƙa biyu, sa'an nan ya tambaya ko shi wane ne, da abin da kuma ya yi.

34. Taron kuwa suka ɗau kururuwa, waɗansu suka ce kaza, waɗansu suka ce kaza. Don tsananin hargowa ma har ya kasa samun ainihin tushen maganar, ya yi umarni a kai shi kagarar sojoji.

35. Da Bulus ya zo ga bakin matakala, sai da soja suka kinkime shi saboda haukan taron,

36. don taron jama'a na dannowa a bayansu, suna ihu suna cewa, “A yi da shi!”

A.m. 21