15. Bayan an yi karatun Attaura da littattafan annabawa, shugabannin majami'ar suka aika musu, suka ce, “'Yan'uwa, in kuna da wata maganar gargaɗi da za ku yi wa jama'a, ai, sai ku yi.”
16. Sai Bulus ya miƙe, ya ɗaga hannu a yi shiru, ya ce,“Ya ku 'yan'uwa Isra'ilawa, da sauran masu tsoron Allah, ku saurara!
17. Allahn jama'ar nan Isra'ila ya zaɓi kakanninmu, ya ɗaukaka jama'ar sa'ad da suke baƙunci a ƙasar Masar, da maɗaukakin iko kuma ya fito da su daga cikinta.
18. Wajen shekara arba'in yake haƙuri da su cikin jeji.
19. Ya kuma hallaka al'umma bakwai a ƙasar Kan'ana, sai ya raba musu ƙasar tasu gādo, suka zauna har shekara arbaminya da hamsin.
20. Bayan haka kuma ya naɗa musu mahukunta har ya zuwa zamanin Annabi Sama'ila.
21. Sa'an nan suka roƙa a naɗa musu sarki, sai Allah ya ba su Saul ɗan Kish, mutumin kabilar Biliyaminu, har shekara arba'in.