2 Tar 9:27-31 Littafi Mai Tsarki (HAU)

27. Sarki ya sa azurfa ta gama gari, kamar duwatsu a Urushalima, ya kuma sa itatuwan al'ul su yalwata kamar itatuwan ɓaure a Shefela.

28. Dawakan Sulemanu, sayo su aka yi daga Masar, da dukan sauran ƙasashe.

29. Sauran ayyukan Sulemanu daga farko har ƙarshe an rubuta su a tarihin annabi Natan. An kuma rubuta su a annabcin Ahaija Bashilone, da kuma a wahayin Iddo maigani, game da Yerobowam ɗan Nebat.

30. A Urushalima, Sulemanu ya yi shekara arba'in yana mulkin dukan Isra'ila.

31. Sulemanu ya rasu aka binne shi tare da kakanninsa a birnin tsohonsa Dawuda, Rehobowam ɗansa shi ya gāje shi.

2 Tar 9