2 Tar 36:1-3 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Jama'ar ƙasa kuwa suka ɗauki Yehowahaz ɗan Yosiya suka naɗa shi sarki. Ya gaji tsohonsa a Urushalima.

2. Yehowahaz yana da shekara ashirin da uku sa'ad da ya ci sarauta, ya kuwa yi mulki a Urushalima wata uku.

3. Sai Sarkin Masar ya tuɓe shi daga sarautarsa ta Urushalima, ya sa su biya gandu, su ba da azurfa talanti ɗari, da zinariya talanti guda.

2 Tar 36