2 Tar 18:8-10 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. Sa'an nan Sarkin Isra'ila ya kira wani jarumi ya ce masa, “Maza ka kawo Mikaiya ɗan Imla.”

9. A sa'an nan Sarkin Isra'ila, da Yehoshafat, Sarkin Yahuza, suna zaune kowa a gadon sarautarsa, kowane ya caɓa ado, suna kuwa zaune a filin da yake ƙofar Samariya. Dukan annabawa kuwa suna ta yin annabci a gabansu.

10. Sai Zadakiya ɗan Kena'ana ya yi ƙahonin ƙarfe, ya ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Da waɗannan za ka sassoki Suriyawa har su hallaka!’ ”

2 Tar 18