2 Sar 4:2-4 Littafi Mai Tsarki (HAU)

2. Sai Elisha ya ce mata, “Me zan yi miki? Ki faɗa mini abin da kike da shi a gida.”Ta ce, “Ni dai ba ni da kome a cikin gidan, sai dai kurtun mai.”

3. Sa'an nan ya ce mata, “Ki tafi ki yi aron tandaye da yawa daga maƙwabtanki waɗanda ba kome a ciki.

4. Sa'an nan ki shiga ɗaki, ke da 'ya'yanki, ku rufe ƙofa. Ki ɗura mai cikin tandayen nan duka, bi da bi.”

2 Sar 4