30. Ka ba ni ƙarfi don in auka wa abokan gābana,Da iko domin in murƙushe tsaronsu.
31. “Allahn nan cikakke ne ƙwarai,Maganarsa tabbatacciya ce!Kamar garkuwa yakeGa dukan masu neman kiyayewarsa.
32. Ubangiji shi kaɗai ne Allah,Allah ne kaɗai madogararmu.
33. Allahn nan shi ne mafaka, mai ƙarfi ne a gare ni,Ya sa hanyata ta zama lafiyayyiya.
34. Ya mai da ƙafafuna kamar na barewa,Ya kiyaye ni a kan duwatsu.
35. Ya horar da ni domin yaƙi,Domin in iya tausa baka mafi ƙarfi.
36. “Ya Ubangiji, ka kiyaye ni, ka cece ni,Taimakonka ya sa na zama babba.
37. Ka hana a kama ni,Ban kuwa taɓa faɗuwa ba.
38. Na runtumi abokan gābana, na kuwa hallaka su,Ban tsaya ba sai da na kore su.
39. Na fyaɗa su ƙasa, ba su iya tashi ba,Suna kwance warwar a ƙafafuna.