1. Wannan waƙa Dawuda ya raira wa Ubangiji sa'ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun Saul da dukan sauran abokan gābansa, ya ce,
2. “Ubangiji ne mai cetona,Shi ne ƙaƙƙarfar kagarata.
3. Allahna, shi ne kāriyata,Ina zaune lafiya tare da shi.Yana kāre ni kamar garkuwa,Yana tsare ni, ya kiyaye ni.Shi ne mai cetona.
4. Na yi kira ga Ubangiji,Ya cece ni daga abokan gābana.Yabo ya tabbata ga Ubangiji!
5. Gama raƙuman ruwa na mutuwa sun kewaye ni,Raƙuman ruwa na hallaka suna gangarawa ta kaina.