2 Sam 13:33-36 Littafi Mai Tsarki (HAU)

33. Don haka, kada shugabana sarki ya damu, cewa, an kashe dukan 'ya'yan sarki, gama Amnon ne kaɗai aka kashe.”

34. Absalom kuwa ya gudu.Sa'an nan sojan da yake tsaro a wannan lokaci ya ga ɗumbun mutane suna tahowa daga hanyar Horonayim, wajen gefen dutse.

35. Sai Yonadab ya ce wa sarki, “Waɗannan 'ya'yan sarki ne yake zuwa, kamar yadda na faɗa.”

36. Yana gama magana ke nan, sai ga 'ya'yan sarki sun iso. Suka yi ta kuka da ƙarfi. Sarki kuma da dukan fādawansa suka yi kuka mai tsanani.

2 Sam 13