1 Tar 21:5-9 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. Yowab ya kawo wa Dawuda adadin yawan mutanen. Jimillar dukan Isra'ila zambar dubu ne da dubu ɗari (1,100,000) waɗanda za su iya yaƙi. Jimillar mutanen Yahuza kuwa dubu ɗari huɗu da dubu saba'in ne (470,000) waɗanda suka isa zuwa yaƙi.

6. Amma bai ƙidaya Lawiyawa da mutanen Biliyaminu ba, domin Yowab bai ji daɗin umarnin sarki ba.

7. Allah bai ji daɗin wannan al'amari ba, don haka sai ya bugi Isra'ila.

8. Sai Dawuda ya ce wa Allah, “Na yi zunubi ƙwarai saboda abin nan da na aikata. Amma ina roƙonka ka gafarta mini laifina, gama na yi aikin wauta ƙwarai da gaske.”

9. Sa'an nan Ubangiji ya yi magana da Gad, annabin Dawuda, ya ce,

1 Tar 21