33. Itatuwa a jeji za su yi sowa domin murnaSa'ad da Ubangiji zai zo ya yi mulki a duniya.
34. Ku yi godiya ga Ubangiji, gama shi nagari ne,Ƙaunarsa madawwamiya ce!
35. Ku ce masa, “Ka cece mu, ya Allah Mai Cetonmu,Ka tattara mu, ka kuɓutar da mu daga al'ummai,Domin mu gode maka,Mu kuma yabi sunanka mai tsarki.”
36. Ku yabi Ubangiji Allah na Isra'ila!Ku yi ta yabonsa har abada abadin!Sa'an nan dukan jama'a suka ce, “Amin, Amin,” suka yabi Ubangiji.