1 Sar 8:11-14 Littafi Mai Tsarki (HAU)

11. har firistoci ba su iya tsayawa su gama hidima ba saboda girgijen, gama ɗaukakar Ubangiji ta cika Haikalin Ubangiji.

12. Sa'an nan Sulemanu ya yi addu'a ya ce,“Ubangiji ya ce zai zauna cikingizagizai masu duhu.

13. Yanzu na gina maka ɗaki maidaraja,Wurin da za ka zauna har abada.”

14. Sa'an nan sarki Sulemanu ya juya, ya fuskanci jama'a suna tsaye, ya roƙi Allah ya sa musu albarka.

1 Sar 8