24. Sai ya umarta a kawo takobi. Da aka kawo takobin,
25. sai ya ce, “A raba ɗan nan mai rai kashi biyu, kowacce ta ɗauki rabi.”
26. Saboda zuciyar mahaifiyar ta ainihi ta cika da juyayin ɗanta, ta ce wa sarki, “Ranka ya daɗe kada a kashe yaron! A ba ta!”Amma ɗayar ta ce, “Kada a ba kowa daga cikinmu, a ci gaba a raba shi.”
27. Sa'an nan Sulemanu ya ce, “Kada ku kashe yaron! Ku miƙa wa ta farin, ita ce mahaifiyarsa ta ainihi.”