23. A kan Yezebel kuwa Ubangiji ya ce, ‘Karnuka za su cinye Yezebel a cikin Yezreyel.’
24. Duk wanda yake na Ahab da zai mutu a birni karnuka ne za su cinye shi, wanda kuma ya mutu a waje tsuntsaye ne za su cinye shi.”
25. Babu wani kamar Ahab da ya ba da kansa ga aikata mugunta a gaban Ubangiji. Matarsa, Yezebel, ita ce ta zuga shi.
26. Ya yi abar banƙyama ƙwarai, ya bi gumaka kamar yadda Amoriyawa suke yi, waɗanda Ubangiji ya kore su a gaban Isra'ilawa.
27. Da Ahab ya ji wannan magana, sai ya yage tufafinsa, ya sa na makoki, ya yi azumi, ya kwanta a tsummokin makoki, ya tashi yana tafiya a hankali.
28. Ubangiji ya yi magana da Iliya Batishbe ya ce,