16. Yanzu dai ina da roƙo guda zuwa gare ki, kada ki hana mini.”
17. Ta ce masa, “To, sai ka faɗa.”Sai ya ce, “In kin yarda ki yi magana da sarki Sulemanu, gama ba zai ƙi jinki ba, ki ce ya ba ni yarinyar nan, Abishag, daga Shunem, ta zama matata.”
18. Bat-sheba kuwa ta ce, “Da kyau, zan yi wa sarki magana dominka.”