1 Kor 6:17-19 Littafi Mai Tsarki (HAU)

17. Duk wanda kuwa yake haɗe da Ubangiji, sun zama ɗaya a ruhu ke nan.

18. Ku guji fasikanci. Duk sauran zunubin da mutum yake yi bai shafi jikinsa ba, amma mai yin fasikanci, yana ɗaukar alhalin jikinsa ne.

19. Ashe, ba ku sani ba, jikinku Haikali ne na Ruhu Mai Tsarki wanda yake a zuciyarku, wanda kuka kuma samu a gun Allah? Ai, ku ba mallakar kanku ba ne.

1 Kor 6