1 Kor 16:5-8 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. Zan zo gare ku bayan na zazzaga ƙasar Makidoniya, don kuwa ta Makidoniya zan bi.

6. Watakila zan jima a wurinku, ko ma in ci damina, don ku yi mini rakiya duk in da za ni.

7. Ba sona ne in gan ku a yanzu in wuce kawai ba, a'a, ina sa zuciya ma in yi kwanaki a wurinku, in Ubangiji ya yarda.

8. Amma zan dakata a Afisa har ranar Fentikos.

1 Kor 16