1 Kor 14:30-34 Littafi Mai Tsarki (HAU)

30. In kuwa an yi wa wani wanda yake zaune wani bayani, sai na farkon nan mai magana yă yi shiru.

31. Dukanku kuna iya yin annabci da ɗaya ɗaya, har kowa yă koya, yă koma sami ƙarfafawa.

32. Annabawa suna sarrafa ruhohinsu na annabci,

33. domin Allah ba Allahn ruɗu ba ne, na salama ne.Haka yake kuwa a duk ikilisyoyin tsarkaka.

34. Sai mata su yi shiru a cikin taron ikkilisiya, don ba a ba su izinin yin magana ba, sai dai su bi, kamar dai yadda Attaura ma ta ce.

1 Kor 14