1 Kor 1:3-8 Littafi Mai Tsarki (HAU)

3. Alheri da salama na Allah Ubanmu, da na Ubangiji Yesu Almasihu su tabbata a gare ku.

4. Kullum nakan gode wa Allah dominku, saboda alherin Allah da aka yi muku baiwa ta hanyar Almasihu Yesu,

5. har ta kowace hanya aka wadata ku a cikinsa, a wajen yin magana duka da ilimi duka–

6. domin kuwa an tabbatar da shaida a kan Almasihu a cikinku.

7. Har ma ku ba kāsassu ba ne a wajen samun kowace baiwar Allah, kuna zuba ido ga bayyanar Ubangijinmu Yesu Almasihu.

8. wanda zai tabbatar da ku har ya zuwa ƙarshe, ku kasance marasa abin zargi a ranar Ubangijinmu Yesu Almasihu.

1 Kor 1