35. Sun tuna, ashe, Allah ne mai kiyaye su,Sun tuna Maɗaukaki shi ne Mai Fansarsu.
36. Amma maganganunsu duka ƙarya ne,Dukan abin da suka faɗa kuwa daɗin baki ne kawai.
37. Ba su yi masa biyayya ba,Ba su yi aminci game da alkawarin da suka yi da shi ba.