16. Ya Allah, sa'ad da ruwaye suka gan ka, sai su tsorata,Zurfafan teku kuma suka yi rawar jiki.
17. Gizagizai suka zubo da ruwa,Aka buga tsawa daga sama,Aka kuwa yi walƙiya ko'ina.
18. Bugawar tsawarka ta gama ko'ina,Hasken walƙiya ya haskaka dukan duniya,Duniya ta yi rawa, ta girgiza, ta kaɗu.