1. Hakika, Allah yana yi wa Isra'ila alheri,Da waɗanda suke da tsarkin zuciya!
2. Amma ina gab da fāɗuwa,Ƙafafuna sun kusa zamewa,
3. Saboda na ji kishin masu girmankai,Sa'ad da na ga mugaye suna arziki.
4. Ba su jin zafin ciwo,Su ƙarfafa ne, lafiyayyu.