1. Ka cece ni, ya Allah!Ya Ubangiji, ka yi hanzari ka taimake ni!
2. Ka sa masu so su kashe ni,A ci nasara a kansu, su ruɗe!Ka sa waɗanda suke murna saboda wahalaina, su koma baya, su sha kunya!
3. Ka sa waɗanda suke mini ba'aSu razana sabili da fāɗuwarsu!