1. Ku yabi Allah da babbar murya ta farin ciki,Ya jama'a duka!
2. Ku raira waƙar darajar sunansa,Ku yabe shi da ɗaukaka!
3. Ku faɗa wa Allah cewa, “Al'amuran da kake aikatawaSuna da banmamaki ƙwarai!Ikonka yana da girma ƙwarai,Har maƙiyanka sukan durƙusa a gabanka don tsoro.