Zab 51:15-19 Littafi Mai Tsarki (HAU)

15. Ka taimake ni in yi magana, ya Ubangiji,Zan kuwa yabe ka.

16. Ba ka son sadakoki, ai, da na ba ka,Ba ka jin daɗin hadayun ƙonawa.

17. Hadayata, ita ce halin ladabi, ya Allah,Zuciya mai ladabi da biyayya,Ba za ka ƙi ba, ya Allah.

18. Ya Allah, ka yi wa Sihiyona alheri, ka taimake ta,Ka sāke gina garun Urushalima.

19. Sa'an nan za ka ji daɗin hadaya ta ainihi,Da dukan hadayun ƙonawa.Za a miƙa bijimai hadayu a bisa bagadenka.

Zab 51