Zab 50:16-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

16. Amma Allah ya ce wa mugaye,“Don me za ku haddace umarnaina?Don me za ku yi magana a kan alkawaraina?

17. Kun ƙi in tsauta muku,Kun yi watsi da umarnaina.

18. Sa'ad da kuka ga ɓarawo kukan yi abuta da shi.Kuna haɗa kai da mazinata.

19. “Kullum a shirye kuke ku hurta mugunta,Ba ku jin nauyin faɗar ƙarya.

20. A shirye kuke ku sari 'yan'uwanku,Ku sa musu laifi.

Zab 50