Zab 39:2-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

2. Na yi shiru, ban ce kome ba,Ko a kan abin da suke da kyau!Amma duk da haka wahalata sai ƙaruwa take yi,

3. Zuciyata kuwa ta cika da taraddadi,Bisa ga yawan tunanina, haka yawan wahalata zai zama,Dole ne in yi ta tambaya,

4. “Ya Ubangiji, kwana nawa zan yi a duniya?Yaushe zan mutu?Ka koya mini ranar da ajalina zai auko.

5. “Ga shi, ka gajerta yawan kwanakina!Yawan kwanakina a wurinka kamar ba kome ba ne.Hakika duk mutum mai rai,Bai fi shaƙar iska ba.

Zab 39